
BY: IBRAHEEM M ALI IBBI
.
Zaune take cikin ofis dinta ta zabga uban tagumi
banda hawaye babu abinda ke shatata afuskarta
kallo daya zakaimata kasan tana cikin tashin
hankali. Abokin aikintane Dr.hafiz yashigo da
sallama turus yayi dayaga halinda take ciki.
Jikinshi yai sanyi sosai yasamu ya zauna kamin
ya saita nutsuwarshi. Aiman aiman dan Allah kiyi
shiru kidaina wannan kukan tunda banga
amfaninshiba kukannanfa ba magani zaiyi mikiba
tomezaisa kita kuka. Cikin wata salahar murya
tace Dr.dole inyi kuka wlh ina mamakin abinda
dadyna ke niyyar yimin saikace wadda bata da
gata koda yake dama haka nataso banida wani
gata saina Allah amma nayi tunanin yanzu
zasubarni hakanan dan hankalina ya kwanta
saigashi sunkuma kawa wani mummunan tashin
hankali cikin rayuwata. Pls Dr.Aiman kiyi hakuri
Dan Allah domin kisami nutsuwa nisainaga kawai
ki kyale komai kikai kukanki wajan Allah ki yadda
da qaddara saikiga kinsami nutsuwa ko kalli
yadda duk kika koma kinrame sosai wlh.
Shikenan nagode Dr.Allah yasaka da alkhairi.
Yauwa kokefa sarauniyar mata. Saida ya rakani
har wajan motata sannan mukai sallama. Rashe
rashe nayi agadona ina maida numfashi.tabe
baki
tayi kamin tace matar mahaukaci ya aikin.wani
murmushin takaici nayi sannan nace
alhamdulillah ina godema Allah daya hadani da
mahauci batare danabi boka ko malamba aikinga
dole ingodema allah. Wani mugun tsaki taja
sannan tabarmin dakin ahankali nafara kuka ina
neman daukin ubangijina domin nasan bemanta
daniba. Hello dady zani wajan mama idan kabari
ba dadewa zanyiba zandan dubatane batajin
dadi. Ok amma karki jima kice ina gaisheta sosai.
Saida nai sallar isha,i sannan nashirya cikin
doguwar riga ta atamfa sannan nadora hijab nai
waje matar dadyna na zaune falo tana taunar
cingam kamar karuwa koda yake meye marabar
dambe da fada. Ga aunty ga aunty cewar
kannena da muka hada uwa daya dasu
rungumarsu naitayi inajin dadi sannan nabasu
tsarabarsu nasamu sukabarni da mama kallona
take cike da tuhuma niko sai zare manyan
idanuna nake kamar antsare makaryaci.
.
Aiman kinada hankali kuwa kinkoga yanda kika
koma.duk kinfige kin lallace wato bazaki yadda
da gaddarabako komifa dayasameki da sanin
Allah jarabawace kisamu ki cinyeta kinji aiman
kiyi hakuri Dan Allah ki kwantar da hankalinki.
Cikin kuka na rungume mahaifiyata mama
kitayani da addua kullun bansamun barci
hankalina yagaza kwanciya mama anya kuwa
dady shiya haifeni kodai nidin diyar wanice ba
dadyba. Karki kuma cewa haka domin mahaifinki
fin karfinshi akai kuma badan komai akai
hakanba saidan hankalina yatashi.amma wlh
nasan dadynki bazaimiki hakaba. Mama ki kalli
tsntsar kyawu da Allah yabani kamar ninayi kaina
babu abinda narasa ajikina Allah yaimin daukaka
nazama babbar likita dukda karacin shekaruna
Allah yaimin farin jini kowa nasan yasame amma
arasa wanda za ahadani dashi sai mahaukaci
mahaukacimma wanda masifar shaye shaye
sabama Allah ya haukatar. Dakin yai shiru sai
sheshshekar kukana datacika dakin. Ki kwantar
da hankalinki ke diya macece zaki iya daukar
kowane hali nada namiji harki saitashi kan yanda
kikeso domin awajanki zai koyi wasu abubuwa
sabida haka ki tsaya tsayin daka wajan ganin
kinshawo kan matsalar gidanki sannan kuma
karki bari kowa yasan sirrin gidanki domin anyine
domin aga yanda zamuyi to aishi Allah ba
azzalumin bawanshi bane Allah yasa hakan shine
kwanciyar hankalinmu. Mama maganar aikina
kuma. Kibarta aiman kiyi hakuri Allah ya
zabamiki
mafi alkhairi cikin rayuwarki. Wayata na ciro
dataketa ring nace mama kingani
mahaifiyarshece
ke kirana. Bayan mungaisane take cewa bazan
gaji da baki hakuriba domin antauyeki da yawa
amma dan Allah kiyi hakuri ki rungumi qaddara
kinji diyata inasonki inasan zama dake kuma
naimiki alkawarin matukar Allah yabawa ammar
lfy kikaji bakisonshi har lokacin to zansa ya rabu
dake domin kisami nutsuwa kinji Allah yaimiki
albarka yashigo dake cikin family dina da SA a
Ajiyar zuciya na sauke mama taimin zuru tana
kallona.domin taji kai.shikenan Allah yasa
mudace cewar mama.
.
Biki akeyi nafada da bada lbr domin mahaifina
hamshakin me kudine haka kuma iyayen angon
nawa. Duk wani wanda ya halarci bikin yasan
naira ta koka. Wani abin mamaki shine babu
amarya babu ango wajan wannan shagalin biki.
Kwance nake inata makyarkyata kan gadona
kanwar mamata tashigo alamun tashin hankali ya
bayyana afuskarta ta zauna gefen gadon tare da
yaye bargon dana rufa dashi sannu Aiman kiyi
hakuri ki kwantar da hankalinki insha Allah
saikinyi alfahari da wannan auran domin
anyishine domin ki wulakanta amma insha Allah
saidai wanda ya shiryashi ya wulakanta domin
babu wanda kika cuta haka babu me cutarki
kidaina kuka kinji. Tashi muje asbt kamin yan
daukarki suzo dan Allah kibar kukannan wlh yana
tashin hankalina sosai ki kwantar da hankalinki
kiba marada kunya kinji Allah yaimiki albarka.
Kwalliya taimin me kyawun gaske nafito
abalarabiyata sak kamar mutun ya saceni dan
kyau ammafa damuwa fal cikin raina domin
fuskatama ta bayyana hakan. Asbt danake aiki ta
kaini magunguna Dr hafiz yahadamin sannan
mukai sallama Bayan sallar isha,i akazo daukata
kukam nashashi kamar wadda tarasa iyaye. . .
Tunsuna lallashina har sukagaji suka kyaleni
ammafa duk wanda ke cikin motar yana cikin
damuwa domin duk yan uwan mamatane wa inda
sukasan ciwona da damuwata. Munsami tara
mekyau da girmamawa daga dangin mijin nawa.
Hakanyasa nadan sami saukin zafin da zuciyata
keyi. Qaton gidane sosai wanda aka kawatashi da
kayan alatu narayuwa. Bangaren hajiyarshi aka
barni harsaida kowa ya watse daga dangina.
Sannan takawomin abinci. Da lemo ammakasa
cinai. Taita mita amma nace mata nakoshi. Wasu
mata nagani wanda na tabbata kannenshine su
biyu halimatu da sadiya yan biyune ko wacce da
goyanta. Suketa nannan dani kamar zasu goyani
komi sunce aunty yayinda nikuma kunya tahanani
sakewa ga mugun zullumin dayake damun
zuciyata na haduwa da mijina shin haukan nashi
na dukane ko jifa ko cizo lallai ina tare da
wahala.
.
Sai wajan 11 nadare umman tace muje narakaki
bangarenki kinji. Zuciyata kamar zatayo waje
sabida zullumin yanda zanganshi wayyoni.
Gaskiya tsarin da akaimin yaimin kyau sosai
domin dady yakashe nera haka mama. Ko zama
banyiba tace wancan saman na mijinkine zo muje
ki Ganshi Dan Allah kiyi hakuri kuyi zamanku lfy
har Allah yakawo ranar dazaisami waraka domin
har yanzu inaji ajikina zai warke shiyasa nakasa
fidda raina ga hakan. Tana rike da hannuna
muka
shiga dakin wayyo Allah saura kadan na sike
sabida zarnin fitsari.yana kwance dagashi sai
gajeran wando kafafunshi nasama yayinda
uwarjikin ke kasa. Ammar ammar ga sabuwar
aunty nakawo maka tashi ka ganta kaji.
Innalillahi wa inna ilaihirraji,un zuwayai ya duka
gabana aunty ina kwana umma taki amsamin.
Wasu hawaye suka zubomin wanda na tabbata
na tausayinshine. Umma meyasameshi haka
naga
kamar rayuwar yara yakeyi. Kwarai kuwa aiman
domin har fitsarin kwance yakeyi hancinki be
jiyemikiba wlh babu asbt dabamu kaishiba
nadaga kasashen duniya amma babu wani cigaba
da akasamu hakanyasa muka zubama sarautar
Allah ido. Kije ki huta zanbaki labarin waye
ammar domin kisami nutsuwar zama dashi
karkije dashi dakinki domin yanada bannar
masifa. Ina komawa dakina nai wanka nai
nafilata
kamar yadda nasaba nai addua sosai kan wannan
jarabawa da Allah yadoramin inafatan yabani
ikon
cinyeta duka. Harna kwanta amma na mike
tausayi yabani yanzunan haka zai kwana cikin
wannan mugun zarni. Kai ina mijinane dole
nakula dashi domin nasan sai Allah ya
tambayemu irin zaman da mukai da mazajenmu
bawai dan besaniba no saidan kafama kanka
shaida. Cikin sanda na nufi dakinshi azuxiyata ina
tsinema wanda yaimai sherin hauka domin cemin
akai shaye shaye ya haukatar dashi. Ina bude
dakin naga yaiwani lama lama barci kawai
yake.nadan bubbugashi cikin muryar kuka
yaiwasu surutai yaci gaba da barcinshi. Dakyar
nasamu yatashi zaune hadda kukanshi bawan
Allah nace zo muje dakina mu kwana kaganan
zarni yakeko nafada ina dode hancina.
.
Lallabashi nayi yabini sannan narufe dakin ina
rike da hannunshi har dakina kai tsaye wajan
mirror dina ya nufa nace inka taba zamu bata
zokai wanka kaji. Hankalinshi nakan kayan
kwalliyar da suka cika mirror din yace aiban
iyaba
nan kawai nake wankewa yanunamin fuskarshi
da
kafafu.kirjina yaiwani dumm auko idan . be
wankaba bazan iya kwanciya dashiba. Taho
inhada maka ruwan sai innuna maka yanda
zakayi. Kamin nahado ruwan harya tube wandon
jikinshi. Aunty inasan wankan yimin da kanki kutt
nakusa suma danaganshi azahirinshi tsaye yana
sosa sumar kanshi. Dakyar nasamu na daidaita
nutsuwata na cire tsoro da fargaba da kunya
nafara wanke jikinshi tass har kuka yake wai zafi
wankan. Wajan shafane naita fama dashi bayan
nagama yimishi shafar saiya samin kuka
waisainaimai kwalliya hakanan nasamu nashafa
miki hoda nakama mishi hannu muje kai fitsari
ka
kwanta inkaji wanima katasheni in rakaka kaji Ko
barcin kirki banyiba sabida zullumin zaimin
fitsarin kwance. Sanda akafara kiran sallah
asbah
yatasheni wai fitsari zaiyi. Dasauri narakashi
yayo
namatsamai mukai sallah tare sannan muka
koma sai lokacin nasami barci.
.
Wajan 9 naji muryar me aikin umma tana sallama
namike ahankali tare da amsawa. Na gaisheta ta
amsa da hanzari hadda dan russunawa domin
batazaci hakaba ganin irin kyawun danake dashi
gakuma dukiya wanda yawancin mata
zakasamesu da wannan mugun girman kan
natsiya. Dama hajiyace tace nakawo muku abinci
gayacan nashirya afalonki. Shikenan nagode sai
anjima zanshigo mu gaisa. Ina komawa naganshi
zaune bakin gadon yanata hamma bako rufe
baki.
Kai ammar kadingasa hannunka kana rufe
bakinka kadda bera yashige maka ko. Saida
nasashi ya wanke bakinshi sannan mukai falo cin
abinci saura kadan nazubar da hawaye domin
yanda yakecin abincin yanayi yana wasa
kamardai yaron da baiwuce shekara huduba.
.
Yai wani kaca kaca da wurin saida nabari
yagama sannan nabashi kayan yamaida kichin
nikuma na gyara wajan. Wani uban zillo yayi
yafado kaina tare dasa kuka.afirgice nace
meyene
me akaimaka bayanshi ya nunamin wai na sosa
mishi Haushi yakamani ohni naga takaina amarya
kenan harna fara aikin megida. Janshi nayi
naimai wanka sosai na gyara sumar kanshi na
aske sajen dayaimai yawa na shafeshi da mai
hadda hoda sannan nace kazaunanan in dauko
maka kaya kaji be kalleniba ya amsa domin jelar
gashina ta daukemai hankali da ita yake wasa.
Karamar riga da wandon jeans na daukomishi kai
haushi waiko wando be iya sawaba. Harna fito
wanka yanata fama yakasa sawa. Saida nagama
kwalliyata sannan nasamishi wayyo gayu inama
ammar lafiyarshi qalau wlh danayi dacen mijin
aure nanuma taro. Shikanshi sai kallon kanshi
yakeyi a mirror yana murmushi. Muje mugaido
umma saimudawo muyi aikin gidako. Washemin
fararan hakoranshi yayi batare dayayi maganaba.
Tsabar mamaki yasata kasa tashi ammafa
bakinta har kunne sabida murna. Kasa naduka
nagaidata sannan shima ya gaidata. Umma
kingani aunty taimin wanka da kwalliya nayi kyau
ko.kunya takamani itako sai murmushi
take.Aiman meyasa baki bari kin hutaba daga
zuwa saiki fara wahala. Haba umma babu wata
wahala wlh. Allah yaimuku albarka yabawa
mijinki lfy. Munjima zaune nace bari mukoma
can
akwai dan gyare gyaren dazanyi. Kibari uwani
tayi miki gatanan zuwa. A a umma tabarshi
kawai.inamikewa shima yamike har yana kokarin
kifawa kasa yabiyoni. Komawa nayi daki nasauya
kayan jikina nanafi dakinshi nai mamakin aikin
dayayi koda yakezuciyarce ta yara ba jikinba
Saida naga dakin yaimin yanda nakeso sannan
hankalina ya kwanta tsalle yaiyafada saman
gadonshi yanacewa inye ansamin sabo dakina
yanayin kanshi.
.
Murmushi nabishi dashi yayinda idanuna suka
kawo kwallah tausayinshi yakamani kai duniya
dole mutun yaji tsoran Allah kuduba lafiyayyan
mutun me tarin kyawu da kwarjini ga ilmi da tarin
dukiya amma lokaci daya Allah ya maida
zuciyarshi ta yara wadda babu komai ciki saitarin
wauta da kuriciya. Munayin sallar azhar muka
kwanta barci domin nai aiki da yawa jikina yagaji
sosai. Dakanshi yatasheni sallar la asar naji dadi
sosai yanzuma saida naimai wanka na nunamishi
yanda zaisa kaya sannan nasamu nashiga nayo
wankan. Muje wajan umma hira yanzu auntyna
kinyi kyau sosai gashinki har baya nima inasan
nawa yayi irin naki. Ammar kadaina cemin aunty
ni kanwarkace kuma matarka kai mijinane
niyakamata na girmamaka bakaiba kaji sunana
Aiman haka zakadinga kirana kaji. Murmushi yayi
kawai bana tunanin yagane wannan dogon
bayanin danaimishi kai gaskiya inajin tausayin
mijina sosai kuma inamishi fatan samun sauki.
Kwance nake nayi filo da cinyarshi.yayinda
shikuma yaketa faman yamutsar gashin kaina wai
ala dole saiyayimin kitso. Umma tai sallama itada
wani matashi abayanta nai saurin tashi zaune
kunya ta isheni. Ammar ya kara shigewa jikina
tare da saka kanshi akirjina yai lamo wayyo
kunya jinai kamar intsaga kasa inshige. Ammar
ga ummafa tazo kaishiru. Kaga hadda bakoma
tazo.banza yaimin.umma tace rabudashi yau
miskilanci nakusa. Aiman ga babban abokin
mijinkinan kuma amini dan uwa. Gafda bikinku
yatafi london sai jiya yadawo dacan shike kulada
ammardin duk da cewa kullun saisunyi fada. Har
russunawa nayi sannan nagaidashi ya amsa cikin
farin ciki da walwala yadora dayimin nasiha kan
muhimmancin aure da irin ladar da zansamu
adalilin rungumar qaddara danayi na zaunada
wanda bashida lfy bayan ina cikin kuruciyata da
kwarjinina. Nan danan mukaita hira har yamma
sannan sukaimin sallama. Mukuma muka koma
dakinmu domin gabatar magriba ina mamakin
sabon da mukayi da ammar domin yanzu ko
kwanciya zanyi saiya rungumeni tsamtsam
ajikinshi.dukda cewa yanadamuna da surutan
shirme amma bana damuwa sam. Satina uku
najema ummanshi da maganar aikina.tace babu
matsala nacigaba da zuwa shisaiya rinka zama
wajanta.nace dashi zandinga zuwa umma domin
ganin mutane da yawama zai debemai kewa
sosai.tai murna tare dasamana albarka sannan
mukayi bangarenmu yana rike da hannuna surutu
yake kamar redio har lumshe idanunshi yakeyi
sabida dadin surutun yakeji qila. Inashiga daki
bayan nagama shirya mana abinda
zamuci.yaiwata banna jikina yayi sanyi binayai da
ido ganin narafka tagumi ina kallonshi tunanina
yanda zan iya gyara wajan. Kamar infasa ihu naji
amma yana iya saida nagama gogemai jikinshi
sannan nafara gyaran wajan gabadaya yabata
wajan da miya da farar shinkafar dana dafamana.
Yana zaune yana kallona na fara aikin wajan
bakinshi be iyayin shiru jinake kamar namakeshi
inhuta. Ihu yafasa tareda cakumata.innalillahi
kasama idonka yaji ko gabadaya yagama rudani.
Dakyar na samu yabude idon sannan najashi
naimai wanka jikina yanata rawa tsabar tsoro
domin aduk lokacinda najemai wanka sainayi
wannan fargabar dalilin ganinshi azahiri gaskiya
daga ganinshi bazaiyima mace hakuriba domin
yana famada kaya.
.
Wani lokacin har addua nake karya warke idan
naga abin nashi. Ga kayanan kasa yanda
nanunamaka kaji inje ingyara falon. Inashiga falo
naji ihunshi da gudu nanufi dakin naikaro da
kujera nakifa dakin naiwani karon dashi goshina
kamar zaitsage sabida zafi. Naisaurin zagemai
ziidin wandon ashewai hadawa yayi da abinshi da
wandan yazage shikenan kayi shiru kaji. Garin
kwashe miyar nazame nafadi wayyo mama
nashiga uku yau wahala zata kasheni Allah kaba
wannan bawa naka lfy konima nasamu sassauci.
Gobe aiki zanidashi ina tunanin karnaje yaitasani
magana ammakuma nasan dole natafi dashi
tunda yariga yasaba dani Shiri mukai bana
wasaba Ammar yayi kyau sosai matukar ba
magana yayiba bazaka gane yarintar tashiba
harkasa hada ido nayi dashi domin wani kwarjini
na musamman dayaimin nashirya cikin kiriyar
atamfa nadora ta aiki sama sannan nasa farin
mayami narikemai hannu muka nufi bangaren
umma. Hawaye kawai tafara tare dasamin
albarka domin ita kanta tana mamakin yanda
yaronta yasauya yadawo Ammar dinshi saidai
tsabar wauta da wasa dakecin ranshi na lalura.
Tai addua taredamana fatan alkhairi narika
hannunshi mukai harabar gidan wani farin ciki ke
cikin zuciyata domin yau zanfita shikanshi cikin
farin ciki yake. Cikin manyan motocinshi nadauki
daya. Kowa murna yake da ganina gyare gyare
nasa akamin sannan nazauna ina hutawa. Bayan
naba Ammar kujerar zama dankarya takurani
duba mutane cikin nutsuwa. Aiman abinci
zanci.dole nabar komai nakoma kanshi nabashi
abaki sannan nacigaba da aikina domin nasan
matukar nace dakanshi zaici to wata wahalar
zaijawomin. Saiwajan uku nasami kaina Dr.Hafiz
yashigo mukafara hirar yaushe gamo Ammar
nagefe yanata wasanshi.Dr.Hafiz yace amma
Dr.kinsan abinda kedamun wannan guy din. Inafa
wlh bansan komaiba kawaidai ummanshi tace
zatabani lbr to kuma har yanzu bataimin
maganarba kasan nikuma bansan takurama wani
shiyasa nai shiru amma wlh abin yana matukar
bani mamaki kadaiganshi mutun har mutun
amma ba tunanin kirki.kasan Allah kusan kullun
sainayi kuka sabida bannarshi to yazanyi nikuma
qaddarata kenan. Kici gaba da hakuri da addua
ammayakamata kiji labarinshi domin kisan ta
yanda zaki temaka mishi. Hakane nagode
Dr.Allah
yabar zumunci agaidamin da madam nakusayin
fishi tunda har yanzu batazo mungaisaba. Bari
mu wuce. Oga tashi mutaiko kinabarka nan.
Murmushi yayi tareda cewa kukazantayi wlh.
Cikin wata biyu naikyau sosai jikina yakara
canzawa.ammafa nadan fada. Yayinda Ammar
yai kiba yakara wani kyau na musamman
hankalinshi kwance yake bashida wata damuwa
kullun dashi nake zuwa aiki dana dawo munyi
abinda zamuyi saimu wuce wajan umma hira
saidare muke komawa. Kannen Ammar nasona
sosai domin suna kuladani yanda yakamata
abangaren ummama bamagana domin tana
gwadamin kauna daidai misali. Yau juma a nida
Ammar muka nufi bangaren umma taimana tarba
ta musamman kamar yadda tasaba muka gaisa
da halimatu da sadiya kannen Ammar sannan
nanemi waje nazauna akan kafet mikar da
kafafuna yayi sannan ya dora kanshi yai
kwanciyarshi yana wasa da yatsun hannuna.
Aiman yauzanbaki lbrin mijinki damu kammu
insha Allah inafatan ba damuwa.kai umma wane
irin damuwa inajinki. Alhaji abdullahi mai yadi
hamshakin me kudine masani kan harkar
kasuwanci Allah yaimishi hannun kyauta da
kaunar talakawa.
.
Matarshi daya hajiya bilkisu tsawon lokaci basu
samu haihuwaba auransu tunna saurayi da
bidurwa amma shiru. Hakan yasa alhaji yafara
neman aure bayan yagayama matarshi hajiya
bilki kuma ta amince domin tasan laifin daga
wajanta take. Alhaji yafara neman aurena
munhadu da alhaji a makarantar danayi ta
scondry domin lokacin yana zuwa wajan
abokinshi dayake shine shugaban makarantar
anan yaganni yanemi shawarar abokinnashi
sannan sukagabatar da kansu wajan yayan
nahaifina da mamata ganinsu manyan mutane
yasa aka amincemusu sukafara zuwa wajena.
Bayan sati biyu da gama makarantana aka
dauramin aure da alhaji. Bansami matsala da
hajiya bilkiba wajan zamantakewarmu har saida
nahaifi Ammar lokacinne alhaji ya maida
hankalinshi gabadaya kanshi. Tun lokacinda na
lura da hakan na tilastama alhaji daina kulada
ammar gaban kowa ammasaiyai biris dani
kawayen hajiya sukaita zuguta harta fara bin
bokaye. Nafara yin barin duk wani ciki danake
dauka bayanna ammar dana haife lfy. Saida nayi
bari shidda sannan Allah yabani cikin yan biyu
babu wanda yasan inadashi domin inajin
alamunshi na matsama alhaji ya maidani gida
domin abin yafara bani tsoro lokacinda nakusa
haihuwa lokacin hajiya bilki tatafi ganin likita
jamany. Agidanmu nahaifi yan biyu alhaji yahada
mana shatara ta arziki saida nai arba'in sannan
muka koma lokacin ammar yanada shekara 11
haka nacigaba da kula da yarana cikin tausayi da
kauna. Daga wannan lokaci bankuma samun
cikiba alhaji yamatsa mukaje asbt wani abin
mamaki shene gaba daya babu mahaifar ajikina
andauketa.babu irin binciken da likitoci basuyiba.
Haka muka dawo har alhaji yafini shiga tashin
hankali nikuwa tuni naima Allah godiya dayasa
masifar tatsaya nan. Ciwon ciki yakama alhaji
cikin dare kamin asuba ya rasu.lokacin ammar
nada shekara 22 yan biyu nada 11 mutuwarnan
ta girgizamu sosai haka muka rungumi qaddara
naci gaba da kula da yarana har muka gama
takaba.har lokacin ana aikin hada dukiyar alhaji.
Sabida rabon gado lokaci haka akazo aka raba
wannan gado gaba daya na ammar yafi nakowa
wannan bakin cikin wannan yasa hankalin hajiya
kin kwanciya. Ko sati biyu ba aiba ammar yafara
shaye shaye da neman mata abin ba arziki
yakoma bejin kunyata bare tsorona.saidai nakan
hana idona barci wajan gayama ubangijina. Haka
yaita facaka da kudi danayi magana yace naki ko
nawa harna daina kulashi domin naga kamar
yanaso yafara zagina abin yana bani mamaki
sosai domin nasan ada ammar baya hulda da
tantiran yara balle haryakaishi lalacewa haka.
Yajima cikin wannan masifa kwatsam kumasai
wannan lalurar tasameshi ahakan so hudu
munamai aure domin babu wani makusancinshi
dazai jurema lalurarshi sai matarshi.amma akayi
rashin sa a kowacce bata wata biyu data dibi
abinda ta diba saitai waje. Maganar magani
kuwa
babu kasar daban kaishiba ammadai duk
maganar dayace shine kwakwalwarshi qalau take
haka komi najikinshi saidai ajira lokacinda
zaidawo daidai. Maganar duniya bata buya domin
kuwa agari naji anata rade raden hajiyace taimai
haka nikuma nasaka sarautar Allah ido domin
nasan da amincewar ubangiji tasami nasara
kuma nima inafatan yabashi lfy. Nasan cewa
bakison ammar kuma suma wa inda suka hada
auran sunyine domin su wulakantaki nasan komai
aiman amma aishi Allah ba azzalimin bawanshi
bane saidaishi bawan yazalinci kanshi.nasan kina
zaune da Ammar dan biyayyar iyayenki to nagode
sosai kuma insha Allah saikinyi farin ciki da
hakan. Idanuna cike da kwalla nace nagode
umma Allah yabashi lfy . Kasa hakuri nayi wajan
11 nadare nakira wayar Dr.hafiz domin shine
abokin shawarata tunda nasan mama natare da
mijinta yanzu. Cikin magagin barci yace Dr.ya
akaine zaki tasheni yanzufa nakwanta ko nauyi
beyiba. Kaga ni dallah karka tashi matarka koma
falo muyi magana nakasa barcin wlh.
.
Inajinki ya akaine amarya.mitsw kaidai kabani
wlh Nan na warwaremai komai hankalinshi
yatashi yace lallai biri yayi kama da mutun wlh
saidanai tunanin haka domin sihiri gaskiyane
kuma yana tasiri akan wanda Allah yaso. To
yanzu meyaka muyi Dr.karki damu kibari saimun
hade Monday sai musan abinyi ko. Yauwa hafizu
nagode sosai Allah yabar zumunci dagaske
goben
zaka kawamin madam din mugaisa. Insha Allah
zaki gammu amma ba zama zamuyiba gidansu
zankaita ta dubo abbanta yayi zazzabi. OK bye.
Lallabawa nayi na kwanta gefenshi.ya rungumoni
hadda sauke ajiyar zuciya tausayinshi yakara
kamani. Watana biyu nagabatarma UMMA
bukatata tasan zuwa gaida iyayena ba musu ta
amsamin ammafa tai jimamin yanda zanbar mata
Ammar gida domin yaiwani irin sabo dani kuma
nikadai ke hanashi ya hanu. To kuma gaskiya
bazanje dashiba yaitamin shirme anamin dariya.
Ran asabar na shirya tsaf na lallaba nabarshi
wajan umma aboye naimata sallama na silale sai
gidan mahaifina domin na tabbata zansameshi
gida yanzu. Cikin tsananin farin ciki yatareni
oyoyo diyata jikinshi na isa ya rungumeni.ina
nane jikinshi muka gaisa yanata murnar ganina
wayyo dadyna nikaina nasan yana matukar
kaunata kawaidai anashiga tsanina dashine
sabida zalunci. Dady aunty batanan ko eh wlh
itada hajiya sukafita yanzu hkama yunwa nakeji
tunsafe sukafita har yanzu banyi break ba.
Dasauri namike wayyo dady sannu ina zuwa cikin
kankanin lokaci nashiryamai abinci sannan
nagyara jikina nakoma wajanshi yanata samin
albarka yabani tausayi sosai koda yake
mahaifiyarshi tajamishi saidai hakuri kawai.
.
Sai wajan azhar nabar gidan nanufi gidan da
mamata take aure. Kannena damuke uwa daya
su hudu aliyu Umar usman sai ummi suka
rungumeni sunata murna nima farin cikin ganinsu
domin inasansu sosai. Nabasu tsaraba sannan
nasamu suka barni da mama. Saida najini
rungume jikinta sannan nasami nutsuwa muka
gaisa tanata tambayata yanayin zaman
banboyemata komaiba. Alhamdulillah ashema ba
mahaukaci bane mutane keta zuzutawa Allah ya
kyauta yabashi lfy. Uhumm naci dariya danaga
mama ta hadomin magungunan mata.kasa hakuri
nayi nace mama yaushe wani abu zaishiga
tsakaninmu akwai yarintafa sosai atare dashi ko
tsarki nina koyamishi. Dakuwa taimin kinci
gidanku to haka zaizauna aidai zaisami lfy ko.
Bayan sallar la asar naduba wayata kiran umma
yakai shabiyar tsoro yakamani da sauri nakirata.
Aiman Dan Allah kidawo hakanan wlh duk
yaimana ta adi yanamu kwanciyar hankali banna
kawai yake yana kuka. To umma ganinan wlh
banji kiran bane. Tuni namike naima mama
bayani da uwargidanta da yake tazo dakin
mamane munata hira zamansu lfy kansu ahade
yake naimusu sallama. Koda nashiga gidan saida
na tsorata duk wani abu na glass saidaya fasashi
ashe hakayake wannan barna. Kuma har lokacin
kuka yake iyakar karfinshi jijiyar kanshi dukta
tashi. Ko kallon inda nake beyiba
Thank's for reading my article
Ameena Part 1Created at 2018-12-09 08:10:52

0
Rate up
Star